KAI MATA A RAGE KISHI GASKIA Al’amarin ya faru ne can cikin - TopicsExpress



          

KAI MATA A RAGE KISHI GASKIA Al’amarin ya faru ne can cikin wani gari dake cikin kasar Niger, Miji ne da matar sa suke zaman lafiya ba tashin hankali tsakanin su, sannan kuma ga soya suna ma juna su. Kwasam daga yace zai kara aure, sai duk wannan biyayyar da take masa da kuma tsabar son da take masa ya gushe. Hmm.. haka dai yaci gaba da hakuri da ita, har Allah yasa yai auren ya kawo Sabuwar amaryar sa fil cikin lallenta. Tsabar kishi yasa uwar Gidan, wata rana akai sa’a ita keda girki a Gidan saboda mijin bai yadda kowace tai nata abin cin bah. Ganin hakane tai amfani da wannan dammar ta zuba masu guba cikin abincinsu shi da amaryar sa. Abin al’ajabi, bayan ya gama cin abin cin nasa, sai ya’yan wannan uwargidan dama su 3 ne duk suka zo suka ci abincin, gaba dayan su, su 5 suka rasu UBA da AMARYA sai kuma YA’YA 3. Mutuwar su yasa matar ta haukace har take fadin abinda ta aikata. Abin tambaya ga mata shine! Shin wai mi kishiya take dashi da kuke kin aimaku ita? Shin shi aure kun manta cewa sunna ce mai girma? Ko kun manta da ayar da tace a auri mace 2, 3, 4 idan mutum bai iya adalci akace ya auri 1? Shin wai baku tuna mutuwa ne? \_____By: #Auwal_kamal_____/
Posted on: Mon, 21 Oct 2013 19:53:29 +0000

Trending Topics



Recently Viewed Topics




© 2015